Ƙaiƙayi ne ke komawa kan mashekiya ga Nasir El-Rufa’i – Baban Chinedu


A cikin wata fira da gidan jaridar Dclhausa tayi da jarumi mawaki na masana’atar Kannywood baban chinedu wanda ya bayyana cewa abubuwan tozarci da gwamnatin nasiru nasir el-rufai ya wuce tunanin mutane.
A cikin zantawar ya bayyana cewa babu ƙasa ɗaya ko jiha da anka galazawa mutane akan cutar korona irin jihar kaduna a shekarar da ankayi wannan cuta duk afrika.
Maganar rusau kuma da kake ji ana fadi na el-rufai ya wuce tunanin mutane , akwai gidajen da sunfi shekara 60 wasu sunfi shekara 40 da sayarwa anyi musu takarda ta gwamnatin jihar kaduna ba ma shi kadai ba.
Wasu da sunka gadi gidajen iyayen su sun mutu suna ciki duk cikin gida ɗaya zaka samu iyali da dangi sama da goma a ƙala suna zaune a wannan wurin alhaji ka tozarta mutum goma 10 , wallahi ko tsuntsaye su yi gidaje ka rushe sai Allah ya jarabce ka.
Akwai maganganu sosai da baban chinedu da zaka saurare su kai tsaye a cikin wanann faifan bidiyo.
Ga bidiyon nan.