Labarai

Abun takaici ne yadda wasu ke murna kan faduwar darajar Naira – Shettima

Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima, ya nuna rashin jin dadinsa game da martanin da wasu ‘yan Najeriya suka yi na murna kan faduwar darajar Naira.

A yayin da yake magana kan kalubalen tattalin arziki da kasar ke fuskanta, Shettima ya soki masu dariyar a matsayin ‘mararsa kishin ƙasa.’

Abun takaici ne yadda wasu ke murna kan faduwar darajar Naira - Shettima
Abun takaici ne yadda wasu ke murna kan faduwar darajar Naira – Shettima

Mahanga ta rahoto a cewarsa “A lokacinda Dala 1 ta koma fiye da Naira 1000 a madadin mu taru mu nuna alhininmu amma abun takaici sai wasu suka riƙa murna a shafin twitter suna jin dadin faruwar hakan. Wannan rashin kishin ƙasa ne” inji Shi.

Wani labari : Najeriya tayi sa’a ba a fara wasa da ni ba – inji Aboubakar

An ruwaito babban dan wasan Cameroon Vincent Aboubakar na cewa sai da ya roƙi mai horas da su akan ya sanya shi tun a farkon wasan Cameroon da Najeriya don yayi maganin Super Eagles amma hakan bai faru ba,

Vincent Aboubakar ya ce “Na roƙi kocina ya saka ni tun a farkon wasan mu da Najeriya a fara wasan dani duk da cewa na dawo daga jinyar rauni amma bai yi hakan ba.

Najeriya tayi sa’a da ba a fara wasa da ni ba…”

A wasan dai an tashi Super Eagles na Najeriya sun ci Cameroon 2 ba ko daya wato Nigeria  2 : 0 Cameroon 

Duk da cewa an sako Vincent Aboubakar a zangon wasa na biyu wato bayan hutun rabin lokaci (Half-time) amma dai duk da haka shigarsa bata sauya komi ba

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button