Labarai

Asia cup 2023: Falasdinu ta kai matakin ƴan 16 a Gasar Asian Cup

Advertisment

Keftin din kungiyar kwallon kafa ta Falasdinu Musab Al-Battat ya bayyana cewa kungiyarsa ta “cika alkawarin da ta dauka ga Falasdinawa” bayan ta kai zagayen sili-daya-kwale a Gasar Cin Kofin Nahiyar Asia a karon farko.

Wasan wanda aka tashi 3-0 wanda suka buga da Hong Kong a ranar Talata shi ne wasa na farko da suka fara ci a gasar kuma ya kai su matakin ƴan 16 a matsayin daya daga cikin huɗu mafi kyau.

Oday Dabbagh shi ne ya kasance gwarzo a Doha inda ya zura kwallaye biyu, sai kuma a usur ɗin ƙarshe da aka busa, sai ƴan wasan Falasdunawa da ma’aikata suka rinƙa mutrna a fili tare da runugmar juna da ɗaga tutoci.

Falasdinu ta kai matakin ƴan 16 a Gasar Asian Cup
Falasdinu ta kai matakin ƴan 16 a Gasar Asian Cup

Jaridar TRT Afrika hausa sun ruwaito cewa, haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta zo ta biyu a rukunin C duk da cewa ta yi rashin nasara a ci 2-1 a Iran.

Nasarar da Falasdinu ta samu a kwallon kafa na zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai mata hare-hare da kuma yin ƙawanya a Gaza.

Ƴan wasa da ma’aikata sun rasa masoyansu sakamakon hare-haren Isra’ila. “Ina so na gode wa duk wadanda suka ba mu goyon baya, “in ji shi.

“Mun yi nasarar sanya murmushi a fuskokin wadanda ke bin mu … ciki ko wajen Falasdinu. Kafin a soma wasan, an yi ta yin ihun “a ba Falasdinawa ‘yanci”.

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button