Ba zan iya auren wanda ba ya son sana’ata ta Wanzanci ba – Hassana Wanzamiyar Dakata
Wata matashiyar mace a kasar hausa wace karamar yarinya ce amma ta dauki kirakin mutane na cewa kowa yabar gida, gida ya barshi to ita dai hassana ta dauki gabon gidansu.
Gidan rediyo freedom radio kano ta samu zantawa da hassana wanzamiyar dakata wacce take ikirarin cewa tabbas duk wanda zai sota dole ne yaso sanatar kamar yadda ta bayyana a cikin wani faifan bidiyo da ake fira da ita.


“Na gadi sanar wamzanci a gurin Babana shima babana ya gada a gurin baban shi, tun ina yar shekara goma mahaifina ya fara nunamin sana’ar Sa’a nan kuma yake zuwa dani domin naga yadda yake yi har na koya na fara domin yanzu ni nake yi da kaina domin bashi da ɗa namiji.
A halin yanzu nakai shekara takwas 8 zuwa tara 9 ina wannan sana’a, yanzu haka kantawa itama ma ina nan ina koya mata.- inji hassana
A halin yanzu har ina zuwa gidan suna, kuma ina ƙaho a fagen aski kuma idan yaro ne nina ke yi amma idan dattijo ne shi yake yi mahaifinta kenan, duba da yanayin rayuwa abubuwa irin reza da sabulu sunyi tsada yanzu ina karba ₦200 amma a can baya naira ₦150 ko ₦100 ne nake karba.- inji hassana
Saurari hirar a nan domin kusha labari daga wanzamiya