Kwankwaso ne ya bude wa APC kofar kwace mulki a Kano – Naja’atu Muhammad


Gidan jaridar Dclhausa sun tattauna da matar nan yar gwagwarmaya kuma mai fashin baki akan abubuwan siyasa da suke faruwa a Afirka ta yamma inda a wannan sati anyi magana da ita ne akan hukuncin da kotu ta yanke a kan zaben jihar kano.
Najaatu Muhammad tayi maganganu da dama sosai akan wannan abun da ya faru wanda tabbas abune da ankayiwa alumma Kano wanda basu ji dadinsa ba.
“Yau idan za’a yi zaɓe saboda Allah in dai za’ayi zabe a gobe a kano zan iya gitta rayuwata Abba ne zai chi zabe a kano”.


Dan jaridar yayi mata tambaya baki ganin irin tarin hujjojinda APC ta tara na cewa tabbas suna da gaskia
“Basu da wata hujja kama karya ce kawai basu da hujja”.
Dan jaridar ya sake cewa ya shugaba tinubu minene alakarsa da abinda kotu tayi akan wannan zabe.
” To ae kowa yasan tsakanin tinubu da Kwankwaso da har yayi masa karya zai bashi minista, lissafi ne kai kwankwaso kasan ba yadda za’ayi kaci zabe kuma kanawa basa son tinubu kowa ya sani, na fada na sake nanatawa idan kuka yadda kuka kassara Atiku kano, ku ka bawa kwankwaso kuri’arku kunka ɓata kuri’,unku sun kace gwanda bata kuri’a.
Kusan kuri’a biyu sunka bata saboda suga tinubu yaci saboda idan atiku ya rasa kano kaman ka bawa tinubu ne kuma abinda ya faru kenan.
Akwai tarin maganganu wanda ku saurari wannan faifan bidiyon domin jin yadda ta kaya.