Wata Mata Ta Jefa Ɗan Autar Kishiyarta A Rijiya A Jihar Katsina


Rundunar ƴan sanda a jihar Katsina ta kama Maryam Habibu, ƴar shekara 18 da haihuwa, bisa zarginta da jefa ɗan kishiyarta mai shekaru hudu cikin rijiya a ƙaramar hukumar ƙafur ta jihar.
Maryam wadda ta fito daga ƙauyen Leko da ke ƙaramar hukumar Ɗanja tare da wasu mutane 11 da ake tuhuma da laifuka daban-daban da suka haɗa da fashi da makami da satar shanu, an gabatar dasu a ranar Juma’a a shelkwatar ƴan sanda da ke Katsina.
Kakakin rundunar ƴan sandan, SP Gambo Isah, yayin da yake zantawa da manema labarai yayin holan, ya bayyana cewa an kama matar ne a ranar 9 ga Nuwambar 2022. Ya ci gaba da bayyana cewar ta fitar da yaron ne ta jefa shi cikin rijiya. Kakakin ya ce Maryam da mahaifin yaron sun rabu.
Manema labarai sun rawaito cewa Maryam wadda ta zanta da manema labaran cikin harshen Hausa, ta amince da aikata laifin, tana mai cewa ƙaddara ce a wasa abun ya faru.
A cewarta, “Gaskiya ne na jefa yaron a cikin rijiyar da ya mutu amma Allah ne ya yi zai mutu a ranar. Shi ya sa ya rasu.”
Wani labari kuma Tabdijam: An kama wata mata anan Arewa ta auri maza Uku duka babu wanda ya sani cikin mazan
Northern Habiscus ta bayar da labarin cewa “Na farko dai tana da shi ainahin uban yaran ta wanda sukayi auren saurayi da budurwa.
Se ta dan samu dan aikin contracts Haka ba a rasa ba a Abuja se take yawan zuwa se ALLAH ya hada ta da wani, da yai mata Fatin Aure se goganiya ta yarda.
Se take musu shift, na garin Su sati biyu na Abuja sati biyu. Duk a cikin Su ba wanda ya Sani.
Can Za tayi tafiya turai ta hadu da wani bayarabe shima yayi ta yin aure ta ce mishi ba matsala aka dada daurawa
Yanzu igiya nawa? Tara kenan ko?
Shi kenan ana nan ana nan, se ta kara haduwa da wani yai mata ta yin Aure har an fara prep se 4th husband yace Bari ya dan bincika shine fa asirin oganiya ya Tonu.
Da ran 4 ya bacci duk se da ya sannar da mazajen hajiya!!! Abu dai beyi dadi ba.