Labarai

Northern Habiscus ‘Malamar Aji’ ta nemi afuwar sheikh Daurawa

Shafin Northern Hibiscus na Aisha Falke wadda aka fi sani da malamar aji ya nemi afuwar Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa kan wallafa hoton a maryarsa.

A saƙon da ta wallafa, Falke ta nemi afuwar malamin inda ta ce, ta wallafa hoton ne don taya shi murna ba don wani abu ba.

Ga abin da ta wallafa a shafinta na facebook

Northern Habiscus 'Malamar Aji' ta nemi afuwar sheikh Daurawa

“Malam ai mana aikin Gafara. Mu murna muka taya ka. Amarya masha ALLAH.

Son kowa kin wanda ya rasa. Daga cikin gidan Su Amaryar aka turo mana suma suna murna, ba Su san ran Malan ze bacci ba. 

Ai malam hada zuriya da kai abin fariya ne, a cikin murna suka turo.

Amarya malam ya ce kin sha kuka, ki dena kuka lokacin farin ciki ne. 

Ayi hakuri 

Anyi kuskure. 

Munai wa malam fatan Alheri “

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=pfbid0ZjypZzX1fYMv79R4cbBFTHkdiUfompdhSpYfvPNhwSdi4Qkd52ktJJ7EZxELvYBAl&id=100052658288897

 

Yanzu haka dai tuni Northern Hibiscus ta cire hoton amaryar Malam din da ta wallafa.

Wannan na zuwa awanni kaɗan bayan da Freedom Radio ta zanta da malamin a kan lamarin.

Malam Daurawa ya gargaɗi masu yaɗa hoton amaryarsa da su daina.

A Jumu’ar nan ne Malam Daurawa zai angonce da Gwarzuwar Alƙur’ani ta ƙasa Malama Haulat Amin Ishaq a birnin Gusau na jihar Zamfara.

 

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button