Buhari ya ci amanar ƴan Najeriya – Naja’atu Muhammad
Fitacciyar ƴar siyasar nan kuma jigo a jam’iyyar APC mai mulki, Hajiya Naja’atu Mohammed ta bayyana cewa shugaba Muhammadu Buhari ya ci amanar ƴan Najeriya musamman al’ummar arewa da su ka zaɓe shi da nufin ya yaƙi cin hanci da rashawa da ya addabi ƙasar.
Hajiya Naja’atu Muhammad wacce tana ɗaya daga cikin waɗanda suka riƙa tallata Muhammadu Buhari a zaben 2015 ta bayyana hakan ne a yau Talata lokacin da ta ke tsokaci akan afuwar da fadar shugaban ƙasa ta yiwa gwamnonin jihohin Plateau da Taraba.
Idan za a iya tunawa dai a makon jiya ne Labarai24 ta rawaito cewa majalisar koli ƙarƙashin jagorancin shugaba Muhammadu Buhari ta sanar da matakin yiwa wasu fitattun ‘yan siyasa da ke kurkuku afuwa kan laifin Rashawa.
Duk da cewa gwamnati a hukumance ba ta fitar da sunaye dukkanin mutanen da ta yi wa afuwa ba, akwai bayanan da ke nuna cewa cikin wadanda aka yi wa afuwa akwai tsohon gwamnan jihar Filato Joshua Dariye da tsohon gwamnan Taraba Jolly Nyame.
Tsofaffin gwamnonin sun kasance cikin mutum 159 da majalisar kolin ta yiwa afuwa wanda aka yankewa hukuncin dauri a gidan yari kan cin hanci da rashawa.
Tun da farko Naja’atu Muhammad ta shaidawa sashen Hausa na gidan rediyon Faransa cewa batun afuwar sam bai dace ba kuma ba ya bisa tafarkin doka.
“Gwamnati ba ta kyauta ba, dan sabo dai ya kamata shi shugaban ƙasa ya gane dukiyar nan ba ta sa ba ce dukiyar al’umma ce”.
“Kuma ita gwamnatin tarayya ba hurumin ta ba ne yin yafiya (Amnesty) ga laifuffukan da su ka shafi jiha, jiha ce ya kamata”.
Ta ƙara da cewa “Buhari ya tabbatarwa da jama’a cewa shi ba mai riƙe amana ba ne kuma shi ba mai tabbatar da alkawari ba ne”.
“Duk alƙawarin da Buhari ya yiwa ƴan Najeriya musamman ƴan arewa da su ka zaɓe shi su ka bi shi su ka rasa rayukansu da dukiyoyin su. Duk amanar da su ka ba shi ya ci ta, babu ɗaya da ya cika”. In ji Naja’atu Muhammad
Wannan gaskiya ne. Buhari yana darewa a gadon mulki yaji yayi daram a Aso ya fara fito da tsiyataku iri iri. Farko dai ya share tsawon 2015 yana ta quni quni sakanin shi da tsoho da duniya Ahmed Joda wai su suna tantance ministoci. Daga karshe sai gashi Buhari ya fito mana da rubabbun mutane a sunan sune ministocin mu. Ya dauki dan jarida ya bashi ministan ilimi. Ya dauki sojan da ake zargin dan giya ne ya bashi ministan tsaro. Wuri uku kadai jama’a suka yi murna da zabin shi, sune; ministan Ayyuka, Ministan Sufuri da ministan Kudi amma sauran duk kwashi kwaraf ne. Sannan fa sai yawon asibiti a kasar waje yayi wata da watanni ya bar kasar mu a Auto Pilot. Koda ya gama watangaririyarsa ya dawo kasar ta tashi daga hannun shi. Su Tunde da Malami da Abba Kyari yan jari hujja sun kwace kasar. Zaman Mamman Daura a Aso Rock bai kari Buhari da kome ba in banda scandals akan scandals. Babban kwabo an dai ji kunya wallahi kun wulakantar da gadon da su Sardauna da Tafa Balewa suka bari. Daga nan sai Buhari ya kulle kunnuwansa da kofofin fadarsa daga mutane masu mutunci, yan alheri, suma suka kaurace masa, suka bar shi da Angulayen da ya kewaye kansa dasu…Kura ta ci Kura. The rest, kamar yadda bature ya ce, is history. Allah Ya saka mana
She is right,, Gaskiya ko da qarfin iko na mulki Ya bashi dama dole ayi duba da irin ta’adi da 6arnar da Suka tafka…. Kafin yi mu Su afuwa…