Labarai

An Dauki Nauyin Karatun Budurwar Da Ta Fara Tattaki Daga Bauchi Zuwa Abuja A Kafa, Tare Da Bata Makudan Kudade

Advertisment

A yau Jumma’a Amira Ahmad ta hadu da dan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a Jam’iyyar APC Farouq Mustapha a gidanshi dake jihar Bauchi.

Idan baku manta ba, a jiya Alhamis “Daily News Hausa” muka kawo muku rahoton Amira Ahmad dake zaune a jihar Bauchi inda ta fara tattaki tun daga jihar Bauchi da niyyar zuwa Abuja domin nuna goyon bayan ta ga dan takarar Gwamnan Jihar a Jam’iyyar APC Farouq Mustapha, tare da karrama ‘yarshi kan namijin kokarin da tayi na shiga cikin tawagar talakawa a yayin taron Jam’iyyar da ya gudana a babban birnin Tarayya Abuja.

Dan takarar Gwamnan ya gaggauta dakatar da budurwar inda ya bada umurnin a dawo da ita gida duba da halin rashin tsaro da ake fama dashi, masu dakatar da itan, sun cimma ta a garin Jos suka dawo da ita gida.

A yau Jumma’a Amira ta hadu da dan takarar yayin ziyarar da ya kawo jihar Bauchi inda ya bata makudan kudade tare da daukan nauyin karatun ta baki daya.

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button