Labarai

YANZU-YANZU: Majalisar Zamfara ta tsige Mataimakin Gwamnan jihar, Mahdi

Advertisment

YANZU-YANZU: Majalisar Zamfara ta tsige Mataimakin Gwamnan jihar, MahdiMajalisar Dokoki ta Jihar Zamfara ta tsige Mataimakin Gwamna, Mahdi Aliyu Gusau.
A zaman majalisar na yau Laraba, ƴan majalisa 20 cikin 21 ne su ka zaɓi a tsige Mataimakin Gwamnan bayan da a ka miƙa ƙudurin cire shi ɗin.
Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa a jiya Talata ne dai kwamitin bincike da a ka kafa domin tuhumar Mahdi ɗin ya zauna jiya, amma kuma Mataimakin Gwamnan bai halarci zaman ba.
Sai dai kuma bayan da kwamitin ya miƙa rahoton da gaban majalisar a yau, sai mambobin su ka zaɓi su tsige Mataimakin Gwamnan.
Ƙarin bayani na nan tafe…

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

One Comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button