[Sautin Murya] Yadda halin yan gudun hijira a Zamfara suke cikin ƙuncin rayuwa
Muna kira ga Buhari da Matawalle da suyi gaggawar kafa wa wadannan mata sannanin ‘yan gudun hijira domin su samu gurin kwana da abinci. Wallahi, Buhari da Gwamna Matawalle ku ji tsoron Allah. Ranar kiyama Allah zai titsiye ku akan hakkin wadannan bayin Allah.
Jama’a mu ji tsoron Allah. Idan mahukunta sun ki sauke nauyinsu, lalle ne mu mu tashi mu yi iya-iyawarmu. Wadannan ‘yan’uwanmu ne, kuma suna da hakki akanmu. Wannan rashin Imani yayi isa haka. Mu ji tsoron Allah.
~ Audu Bulama Bukarti”
“A matsayinka na ɗaya daga cikin mahukunta wannan jaha;
– Shin a wannan hali kana iya barci kuwa?
– Shin kana iya murmushi har da dariya?
– Kana amfani da kuɗin wannan jaha wajen biyan naka buƙatu da iyalinka?
A haka yadda ake tafiya a naka tunani babu wata matsala ko wani sakamako ko alhaki da zai biyo baya?
Kana tsammanin shi ke nan za a cigaba da tafiya a haka kuma kai ka zauna lafiya kai da iyalanka babu wani hukunci, jarabawa, musiba ko biyan bashin alhaki daga Ubangiji?
Anya?!
– Abubakar Sadiq”
Ga sautin murya hira da bbchausa tayi da su nan ku saurara.