Wasu hotunan Rahama Sadau A Wajen Daukar fim a India sun janyo cece kuce
Rahama Sadau ta kasance fitacciyar jaruma a kannywood wadda take da dunbin masoya da dama daga fadin kasashen duniya zuwa kasarmu ta Nigeria jarumar ta kware wajen wasan kwaikwayo saboda duk fitowar da tayi a fim tana fito yadda yakamata domin bada gudunmawa
Sede jarumar Tasha janyo abubuwan da suke janyo cece kuce wanda jarumar ta zama ta farko a kannywood a bangaren janyo wa masana’antar kannywood zagi da tsinuwa domin irin abinda take janyowa harkar ta fina finai
Jaruma Rahama Sadau rayuwar turawa takeyi bata damu da abinda al umma zasu fada akanta ba ko kadam domin kuwa tanayin shigar data ga dama babu ruwanta tasa kayan da sukayi mata ko a jikinta wanda ko kwanan baya nasan baku manta cece kucen da jaruma ta janyo ba wanda har takaiga abokan sana’arta sun raba kansu da ita.
Anan kuma wasu hotuna muka samu na jarumar bayan shigarta masana’antar shirya fina finai ta kasan india inda take daukar hoto tare da ma’aikatan wannan fim din da suke gaba tarwa a india a cikin hotunan data wallafa a shafin nata jarumar sun nuna yadda yan kasar suke rabarta tare da daura mata hannu a kafada.ga hotunan nan kasa.