Labarai

Mace ta cinna wa kanta wuta a Jigawa ‘saboda mijinta zai ƙara aure’

Advertisment

Wata mata mai suna Maimuna Wadaji ta cinna wa kanta wuta da zummar kashe kanta da kanta saboda mijinta zai ƙara aure, a cewar ‘yan sandan Jihar Jigawa da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Lawan Shiisu, ya faɗa wa kamfanin dillancin labarai na NAN cewa matar ta aikata laifin ne a ranar Juma’a da ta gabata a ƙauyen Runguma na garin Dutse, babban birnin jihar.

Kamar yadda bbchausa na ruwaito. Ya ce Maimuna ta yanke shawarar aikata hakan ne bayan ta samu labarin cewa mijin nata zai sake auren tsohuwar matarsa.

“A ranar Juma’a da misalin 10:00 na safe, ‘yan sanda sun samu labarin wata mai suna Maimuna Wadaji…ta yi yunƙurin kashe kanta, inda ta zuba man fetur sannan ta cinna wa kanta wuta,” a cewarsa.

“Daga baya kuma ta yi ihun neman taimako, abin da ya sa aka garzaya da ita asibitin Koyarwa na Jami’ar Dutse (FUD) don yi mata magani.”

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button