Labarai

Dukda Gwamnatin Ku ta Haramta amma zamu taimaka maku kuci Gaba da shiga Twitter Kuna anfani da ita ~Inji Kwamfanin Twitter

Advertisment

kamfanin yada labarai na Microblogging na Twitter sun bayyana shirinsu na taimakawa ‘yan Najeriya samun damar shiga dandalin na Twitter duk da cewa gwamnatin Najeriya ta hana.
A cikin wata sanarwa a ranar Juma’a, ministan sadarwa na Najeriya Lai Mohammed ya sanar da dakatarwar, dangane da wannan shawarar da kasar ta yanke, Twitter ta wallafa a shafinta na manufofin cewa za su yi aiki don dawo da damar ga dukkan ‘yan Nigeria, Kamar yadda jaridar mikiya na ruwaito.
Mun damu matuka da toshewar shafin Twitter a Najeriya. Samun dama kyauta na Shiga #OpenInternet hakki ne na ɗan adam a cikin zamantakewar zamani.
“Za mu yi aiki don dawo da dama ga duk wadanda ke Najeriya wadanda suka dogara da Twitter don sadarwa da cudanya da duniya. #KeepitOn, “kamfanin ya sanya wannan a yau ranar Asabar.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button