Labarai

Caccakar Buhari: DSS ta cafke hadimin Ganduje, Dawisu, bayan yace APC ta gaza

Advertisment

Hukumar tsaro ta fararen kaya (DSS) ta damke Salihu Tanko-Yakasai, mai magana da yawun gwamna Kano, Abdullahi Umar ganduje bayan ya ce gwamnatin APC ta gaza.
A ranar Juma’a, Tanko-Yakasai ya bayyana damuwarsa a kan labarin kwashe yara mata na makarantar sakandaren kwana da ke Jangebe a jihar Zamfara
 
 
 

 
Bayan sa’o’i kadan da yin tsokacin a shafinsa a Twitter, an nemi Yakasai ko kasa ko sama an rasa, Legit ta wallafa.
Amma a wata wallafa da shafin Twitter na jihar Kano yayi, an sanar da cewa Tanko-Yakasai na tare da jami’an tsaron farin kaya.
A wallafar da Yakasai wanda aka fi sani da Dawisu yayi a shafinsa na Twitter bayan samun labarin satar ‘yan matan daga makarantar Jangebe, ya bukaci gwamnatin APC da ta kawo karshen ‘yan ta’adda ko tayi murabus.

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button