Kannywood

Gaskiyar Labarin Makancewar Jaruma Shehu Hassan Kano ?~ Shehu Hassan Kano

Fitacce jarumi, kana kuma jigo a masana’antar (Kannywood) Alhaji Shehu Hassan Kano, ya musanta raɗe-raɗin da ake yaɗawa cewar wai “ya makance ba ya ganin komai da idanuwansa”.
Shehu Hassan Kano ya musanta labarin makancewar tasa ne a ya yin zantawarsa da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta wayar salula a wannan rana.
Shehu Hassan Kano ya kuma ƙara da cewa a kwanakin baya ya yi rashin lafiya wacce ta kai ga an yi masa aikin ido, ba wai makancewa ya yi ba, kuma ko a yanzu haka ya na ganin komai rangaɗaɗau da idanuwansa har ma ya na iya gani da karanta rubutu ba matsala.
 
 
 
A ƴan kwanakin da su ka wuce an yi ta yaɗa jita-jitar cewa Shehu Hassan ɗin idanuwansa sun samu matsala har ma ba ya iya gani da su, ya yin da a wannan rana ya tabbatarwa da jaridar Dokin Ƙarfe TV cewa wancan labarin ba gaskiya ba ne ya na gani.

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

3 Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button