Gwamna Zulum ya ziyarci kauyukan Gwoza, ya raba kayan abinci Da N24m ga ‘yan kasa 1200 masu rauni (Hotunan)
A cikin ziyarar ya lura da gidaje 350, wasu a Ngoshe, Warabe, Pulka..
Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya kwashe yininLitinin don raraba kayan abinci a Ngoshe, Warabe da Pulka, duk a Karamar Hukumar Gwoza da ke Kudancin Borno.
A Ngoshe, Zulum ya lura da rabon kayan abinci da N24m a tsabar kudi ga ‘yan kasa 1,200 marasa karfi wadanda suka dawo daga Pulka da Maiduguri.
Kowane magidanci ya samu buhun masara mai nauyin 50kg, buhu 1 na dawa 50kg, buhun wake 25k, buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 12.5, lita 5 na man girki, sauran kayan miya da kuma kudi N20,000.
Rabaran, Zulum ya ce, ya kasance yana ci gaba da tallafawa al’ummomin da aka tsugunar da su kafin lokacin damina wanda ana sa ran za su gudanar da ayyukan noma cikin aminci a filayen noma a matsayin wani bangare na inganta rayuwar su.
‘alumma sun koma Ngoshe a ranar 15 ga Oktoba 2020, bayan samun umarni daga rundunar sojoji.
Gwamna Zulum ya kuma duba abubuwan more rayuwa bayan haka ya umarci Hukumar Kula da Ilimin Firamare ta Jiha da ta hanzarta samar da kayan daki tare da tabbatar da bude Makarantar Firamare ta Ngoshe ta Tsakiya cikin makonni biyu. Aikin makarantar yanzu yana matakin kammala kashi 95 cikin ɗari.
Haka kuma gwamnan ya ziyarci cibiyar kula da lafiya ta matakin farko ta Ngoshe inda ya umarci dan kwangilar da ya hanzarta kammalawa domin baiwa ma’aikatan lafiya damar samar da aiyuka ga al’umma.
Bayan tashi daga Ngoshe, Gwamna Zulum ya tafi Warabe shima a Gwoza kuma ya duba gidaje 350 da ake ginawa ga mazauna wadanda maharan suka rusa gidajensu.
Zulum ya kuma ziyarci Pulka inda ya duba yadda ake gina babbar makarantar sakandare.
Voice of Borno……..