Labarai

Zarar Bunu: Ganduje Ya Dakatar Da Salihu Tanko Yakasai Sakamakon Sukar Gwamnatin Buhari

 
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya dakatar da mai taimaka masa na musamman a kan kafafen yaɗa labarai Salihu Tanko Yakasai, sakamakon sukar gwamnatin Shugaba Buhari, in da ya bayyana gwamnatin a matsayin wacce ba ta tausayin ‘yan Najeriya.

Wannan shine abinda wannan hadimin na ganduje ya wallafa a twitter dinsa

 
Sanarwar dakatarwar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Malam Muhammad Garba ya sanyawa hannu.
 
Sanarwar ta ƙara da cewa a matsayin Salihu Tanko Yakasai mai riƙe da muƙamin gwamnati abu ne mai wahala a banbance tsakanin ra’ayinsa da kuma ra’ayin gwamnati.
Haka kuma sanarwar ta ce matakin dakatarwar ya fara nan take.







Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button