Buhari ya ce soke SARS matakin farko ne na sauya fasalin aikin ƴan sanda a Najeriya
A karon farko shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya fito ya yi wa ƴan ƙasa jawabi kan soke rundunar ƴan sanda ta Sars.
Shugaba Buhari ya ce soke rundunar matakin farko ne a sauye-sauye masu tsauri da zai aiwatar kan aikin ƴan sanda domin tabbatar da cewa jami’an tsaro sun yi aikin da ya dace da kare rayuka da dukiyoyi.
Buhari ya ce gwamnati ta damu da ƙorafin ƴan Najeriya kan amfani da ƙarfi sama da kima da ƴan sanda ke yi a wasu lokutan da kuma kisa mara dalili.
The disbanding of SARS is only the first step in our commitment to extensive police reforms in order to ensure that the primary duty of the police and other law enforcement agencies remains the protection of lives and livelihood of our people. pic.twitter.com/XjQMSr3jlm
— Muhammadu Buhari (@MBuhari) October 12, 2020
Jawabin shugaban na minti ɗaya da rabi a shafin Twitter ya ce gwamnati za ta tabbatar duk wadanda ake zargi ko da hannu a cin zarafi su fuskanci shari’a.
Sannan ya nuna takacinsa kan mutuwar mutum guda a jihar Oyo a yayin zanga-zangar #EndSars, kuma ya umarci a gudanar da bincike kan musababin mutuwarsa.
Shugaban ya ce aikin ɗan sanda shi ne kare ƴan ƙasa don haka ba za a lamunci wasu kalilan ko ɓata gari su kasara kimar aikin jami’an tsaro a Najeriya ba.bbchausa ne ta ruwaito.