Labarai

Duk Wanda Aka Kama Da Laifin Fyade za’a Dandaƙeshi kuma A Kasheshi (Hotuna) ~ Nasir El-rufai

Advertisment

Maigirma gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya sanya hannu a sabuwar doka na yin dandaka da kisa ga duk wanda aka kama da laifin fyade

Dokar na cewa:
Duk wanda yayi wa yarinya ‘yar kasa da shekara 14 fyade to za’a dandake shi, sannan a kashe shi

Duk wanda ya yiwa matar da ta haura shekaru 14 fyade za’a dandakeshi, sannan zai tabbata a gidan yari har karshen rayuwarsa, wato daurin rai da rai

Advertisment

Duk macen da ta yiwa namiji yaro fyade to za’a yi mata tiyata a cire kwayar halittar dake samar da koyin haihuwa a jikinta, wato itama za’a dandaketa

Duk yaron da bai balaga ba, ya yiwa yarinya fyade, za’a kama yaron a masa rijista cikin masu laifin cin zarafin mata, sannan za’a daukeshi a hoto a yadashi a kafofin watsa labarai da na sada zumunta ta yanda har abada duniya zata kalleshi a matsayin wanda ya taba aikata laifin fyade

Jinjina ga Maigirma gwamnan jihar Kaduna, Insha Allahu da wannan dokar muna sa tsammanin karshen masu aikata laifin fyade yazo a jihar Kaduna, muna fatan sauran gwamnoni zasuyi koyi da shi

Allah Ka kawo mana karshen wannan masifa na fyade Amin

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button