Labarai

Buruji Kashamu: Cutar korona ‘ta kashe Tsohon Sanatan Najeriya’

Advertisment
Tsohon sanata mai wakiltar Ogun ta gabas a Najeriya Buruji Kashamu ya mutu.
Sanata Ben Murray-Bruce ne ya tabbatar da mutuwar abokin nasa a shafinsa na Twitter inda ya ce cutar korona ce ta kashe tsohon sanatan.
A saƙon da ya wallafa, ya ce Sanata Kashamu ya mutu ne a asibitin First Cardiology Consultants, wanda a asibitin ne Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Najeriya Abba Kyari ya mutu.
Kauce wa Twitter, 1

Karshen labarin da aka sa a Twitter, 1
Kafin mutuwar Sanata Kashamu, ya kasance ɗan majalisar dattijai mai wakiltar Ogun ta gabas.
Ya kuma kasance ɗan takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar PDP a 2019 a jihar Ogun.jaridar bbchausa na ruwaito.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Advertisment
Back to top button