Uncategorized

Da duminsa: Gwamnatin tarayya Ta Rage kudin Aure a Najeriya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta rage kudin gudanar da aure a Najeriya. Sabon kudin da ta sanya zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuli.

Sabon kudin ya zo karkashin dokar aure ta CAP M6 LFN 2004, a cewar sanarwar da babban sakatare kuma mai rijistar aure a Najeriya, Georgina Ehuriah.

Wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ma’aikatar cikin gida ta Najeriya, Mohammed Manga, ta bayyana cewa hakan wani garambawul ne da gwamnati za tayi a fannin auren bayan samun shawarwari daga masu ruwa da tsaki a kwanan nan.

Lasisin yin aure a wuraren bauta an rage shi daga N30,000 na tsawon shekara biyu zuwa N6,000 a kowacce shekara.

Sabunta lasisin auren a wajen bauta, an amince a dinga biyan N5,000 a kowacce na tsawon shekara uku. Yayin da a da yake N30,000 kowacce shekara.

Hakanan an rage kudin daurin aure daga N21,000 zuwa N15,000, inda aka rage kudin lasisi na musamman daga N35,000 zuwa N25,000.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button