Da duminsa: Gwamnatin tarayya Ta Rage kudin Aure a Najeriya
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta rage kudin gudanar da aure a Najeriya. Sabon kudin da ta sanya zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuli.
Sabon kudin ya zo karkashin dokar aure ta CAP M6 LFN 2004, a cewar sanarwar da babban sakatare kuma mai rijistar aure a Najeriya, Georgina Ehuriah.
Wata sanarwa daga daraktan yada labarai na ma’aikatar cikin gida ta Najeriya, Mohammed Manga, ta bayyana cewa hakan wani garambawul ne da gwamnati za tayi a fannin auren bayan samun shawarwari daga masu ruwa da tsaki a kwanan nan.
Lasisin yin aure a wuraren bauta an rage shi daga N30,000 na tsawon shekara biyu zuwa N6,000 a kowacce shekara.
Sabunta lasisin auren a wajen bauta, an amince a dinga biyan N5,000 a kowacce na tsawon shekara uku. Yayin da a da yake N30,000 kowacce shekara.
Hakanan an rage kudin daurin aure daga N21,000 zuwa N15,000, inda aka rage kudin lasisi na musamman daga N35,000 zuwa N25,000.