Labarai

Shugaban Buhari Ya Bada Umarni A Gama Da Yan Ta’addan Da Suka Addabi Katsina

Advertisment

Daga : Datti asaalafy

Maimagana da yawun shugaban Kasa Muhammadu Buhari Maigaskiya Malam Garba Shehu ya fitar da sanarwan cewa shugaba Buhari ya bada umarnin daukar matakin soji a kan ‘yan ta’addan da suke ta’addanci a jihar Katsina

An tura rundinar sojoji mayaka na musamman kwararru cikin sirri zuwa wasu manyan sansanin ‘yan ta’adda da aka gano a jihar Katsina. a sanarwan da Malam Garba Shehu ya fitar, kuma yakin zai kasance cikin sirri ne

Shugaba Buhari ya nuna bacin ransa da matukar damuwa bisa halin da aka shiga na tabarbarewan tsaro a jihar Katsina, ya bawa sojoji umarni su kakkabe dukkan wata maboya na ‘yan ta’adda a jihar, yakin zai kasance da taimakon sojojin kasa da sama da ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro

Muna rokon Allah Ya sa wannan mataki da shugaba Buhari ya dauka ya zamto sanadin kawo karshen ta’addancin da akeyi a jihar Katsina

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button