Labarai

Shugaba Buhari Ya Amince Da Samar Da Sabbin Kwalejin Ilimi Na Tarayya (FCE) A Jihohi Shida

Advertisment

Daga Salisu Magaji Fandalla’fih

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bude sabbin kwalejin horon malamai guda shidda; daya a kowanne bangare 6 na kasa.

Hadimin shugaban kasa, Bashir Ahmad, ne ya tabbatar da hakan a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter.

FLASH: President Muhammadu Buhari has approved the establishment of six new federal colleges of education in each of the six geo-political zones of the country.

•Bauchi
•Benue
•Ebonyi
•Osun
•Sokoto
•Edo

— Bashir Ahmad (@BashirAhmaad) May 14, 2020

Za a samar da sabbin Kwalejojin ne a jihohin Bauchi, Benuwe, Ebonyi, Osun, Sokoto da Edo.

A wata takarda kuma da ta fito mai dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar ilimi, Sunny Echono, ya ce an tsayar da ranar 11 ga watan Mayu domin ziyartar wuraren da za a bude kwalejojin a jihohin.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment








Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button