Labarai

Yanzu-yanzu: Yan Shi’a sun bankawa ma’aikatar NEMA wuta

A yanzu haka, wani sashen ma’aikatar hukumar bada agaji na gaggawa ta kasa wato NEMA dake Abuja na ci bal-bal.

Hakazalika an bankawa motocin hukumar biyu wuta kuma jami’an kwana-kwana na cikin kashe wutan yanzu.

A cewar The Cable, Wani mai idon shaida ya bayyanawa manema labarai cewa yan kungiyar Shi’a mabiya Sheik Ibrahim El-Zakzaky da suke gudanar da zanga-zanga suka bankawa ma’aikatar wuta lokacin da yan sanda suka hanasu zanga-zanga.

Zanga-zangar wacce suka fara daga tashan NITEL Junction dake Wuse 2 ya samu cikas ne yayinda yan sanda suka toshe hanyar zuwa majalisar dokokin tarayya da fadar shugaba kasa

Kawai sai yan sanda suka fara harbe-harbe yayinda yan Shi’an ke kokarin shiga farfajiyar Eagle Square. Akalla mutane biyu sun rasa rayukansu kawo yanzu.

Wani dan Shi’a yace: “Za mu cigaba da zanga-zanga, kuma idan basu son ganinmu a kan titi, gwamnati ta saki shugabanmu. Idan suna son kashe, su cigaba da kashemu.”

Gawar da anka kashe

Ga bidiyo
HAPPENING NOW: National Emergency Management Agency (NEMA) shed/outpost set ablaze by Shi’ite members in Abuja. pic.twitter.com/UJiFseMPWc

— TVC News (@tvcnewsng) July 22, 2019

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button