Labarai

Kwankwaso ya samowa Dalibansa Gurbin Karatu a Jami’ar Mewer dake Kasar India

Advertisment

Daga Khadija Garba Sanusi

 A yammacin yau ne Laraba 10/7/2019 Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya kammala samarwa wasu daga Cikin Dalibai 370 yayan talakawa Gurbin karatu a Jami’ar MEWER UNIVERSITY dake Kasar India akan fannonin Daban-daban na ilimi Wanda Gidauniyar sa ta KWANKWASIYYA DEVELOPMENT FOUNDATION zata dauki nauyinsu zuwa kasashe daban-daban na Duniya.

 zuwa yanzu dai Kwankwaso ya ziyarci Jami’o’i guda biyu akasar ta India a Cigaba da zagayen nemawa Daliban gurbin karatu da yakeyi akasashen Duniya a kakar karatu ta bana Wato (2019/2020 Academic Session).

 Sanata Kwankwaso Yana tare da Rakiyar Jagoran Kwankwasiyya na Jihar Kebbi Eng. Abubakar Sadiq Argungu.

Kwankwasiyya Reporters Nigeria

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Check Also
Close
Back to top button