Labarai
Ganduje Na Abuja Don Neman A Cire Kwamishinan ‘Yansandan Jihar Kano
Biyo bayan takaddama a zaben gwamnan jihar Kano, Gwamna Ganduje ya yi tattaki zuwa Abuja don Neman a cire kwamishinan ‘yansanda na jihar, Muhammad Wakili.
Majiyarmu ta Daily Nigerian ta bayyana cewa Muhammad Wakili ya yi kokarin daidaita lamura a lokacin zaben gwamna a jihar Kano.
Bayanai sun nuna gwamnan ya samu rakiyar shugaban majalisar dokokin jihar Kano, Kabiru Rurum da shugaban jam’iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com