Labarai

“Burina Na Saita Nijeriya Kan Tafarkin Da Al’umma Za Su Ji Dadi” JAWABIN SHUGABA BUHARI

Advertisment

“Ubangiji Ya san zuciyata, ba ta da wani buri da ya wuce na sai ta kasata Nijeriya, a tafarkin da za ku ji dadi nan gaba, domin kune matasa masu tasowa.

Akwai tsananin wahala a mulki, yayin da kake koqarin kawo canji a kasa Kamar Nigeria, Zaka hadu da Kalubale Kala Kala mai Wahalar gaske.

Muna iya kokarinmu a yanzu domin mu ga komai ya daidaita a kasar mu, kuma na tabbata koda abokan hamayyar mu sunsan cewa muna iyakar kokarimu don ganin mun daura kasarmu a turbar data dace.

Amman na san wasu daga cikinsu suna ganin mun yi laifi, sakamakon hana ha’inci da almundahana da dukiyar al’umma.

Ga wadancan ‘yan siyasa, masu sha’awar abarsu suyi wadaka da kudin gwamnati mun san bazasu ta6a yafe mana ba Ko kuma su ga kokarinmu. Ba za su gani ba.

Domin ana su tunanin ba mu kyautata musu ba, mun yi musu laifi, laifin kuwa shine:-
Mun toshe musu duk wassu hanyoyin dasuke bi wajen sace dukiyar al’ummah. Dominsu
basu da wata damuwa, illa abarsu suyi badakala da dukiyar kasa.

Sun yarda da haka koda kasarnan zata lalace, domin suntara kudaden da gidaje a ketare.

Sun shirya tsaf da karfinsu domin wargaza shirin da muka soma na saita wannan kasar tamu, basu da damuwa koda da kwayar zarra, dangane da damuwar mutanen kasar nan .
Bamu da wani za6i, Illa za6in mutanan Nijeriya, idan sun amince da kokarinmu, zasu iya sake za6anmu a karo na biyu domin cigaba daga inda muka tsaya, Hakanne zai amfanemu Baki daya.

Idan kuma baku aminta damu ba, zaku iya komawa garesu ba (wato yan jari hujja ). Domin wargaza muku rayuwar ku ta nan gaba, dama kasar baki daya.

Amma na tabbata zaku tuna cewa na fada muku gaskiya ko bayan Raina, kuma nayi iya kacin kokarina domin naga kasarmu ta hau turban gaskiya, da rikon amana, Za6i ya rage naku ‘yan Nijeriya. domin kasarmu.

Allah ya san zuciyata da abinda ke cikinta, inayin wannan maganane tsakanina da Allah.

ALLAH YA TAIMAKI KASATA DA AL’UMMARMU BAKI DAYA.”

Daga Umar Bandi Kofar kware

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com
Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button