Kannywood

Rayuwar Matan Arewa Cike Take Da Kalubale – In Ji Jaruma Rahama Sadau

Advertisment

Daga Habu Dan Sarki

Jarumar Hausa Fim Rahama Sadau ta bayyana cewar, rayuwar yar Arewa mai hankoron zama wani abu nan gaba cike take da cikas iri-iri.

Sadau ta yi wannan batu ne a tattaunawa ta da jaridar Thisday. Jarumar ta ce dakatar da ita da aka yi a harkar fim din Hausa ya janyo ta sake samun wasu sabbin hanyoyi a harkar fim na cikin gida da waje.

Jarumar ta ce a kullum tana kokari wajen kare mutuncinta da kuma al’adarta a lokacin da take harkar sana’ar fim na turanci wanda aka yi a kudancin Nijeriya.

Sadau ta ce ko cikin kwanakin nan ta ki amincewa da yin wani fim na turanci wanda aka bukaci ta fito a matsayin ‘yar madigo.

Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Advertisment






Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button