Uncategorized

Masu waziri:Hattara kada kilu ta jawo Bau!|Dr.sani umar r/lemo

Masu Wa’azi: Hattara Kada Kilu Ta Jawo Bau!:
“Wani labari mai ban takaici da ya faru na wani mai wa’azi, yayin da wata rana wani ya zo ya fada masa cewa, ‘Mawakiya Muniarah Al-Mahdiyya ta bude wasannin rawa da waka a dandalin Abbasiyyah”. Sai mai wa’azin nan da ya zo wa’azinsa a masallacin juma’a na “Al-Jami’ul Umawi” ya fusata ya rika yana cewa, ‘Yaya za a yi mace ta fito da jikinta waje a gaban maza tana tikar rawa, tana nuna tsiraicinta. Ina masu kishin addini suke da ba su yi komai akai ba?’.
Sai jama’a suka rika cewa, ‘A’uzu billahi! A ina wannan abu ya faru? Kuma da yaushe hakan ta auku?. Sai mai wa’azi ya kada baki a fusace, yana fada musu, ‘Ai a dandalin Abbasiyya ne abun ya faru, kuma dadaddare bayan sallar isha’i’.
Lokacin da abun ya faru, dududu jama’ar da suka halarcin wasan ba su fi rabin dakin taron ba. Amma bayan da wannan mai wa’azi ya gama wa’azinsa, sai ga shi ‘daikin taro’ ya cika makil da ‘yan kallo.
Wannan lamari da ya faru, ya kamata ya zama darasi da izina ga masu kuzuzuta ayyukan ta’asa cikin wa’azinsu, wanda hakan daga karshe yake komawa ya zama talla da kiran-kasuwa ga wannan laifin, cikin rashin sani”. – As-Sheikh Ali At-Tantawi, a cikin littafinsa “Zikrayaat”, juzi’i na 1, shafi na 53.
Mun Dauko Daga Shafin Hausaloaded.com

Mr HausaLoaded

Abubakar Rabiu Editor-in-cheif

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button